Dä DUMIDUMINSA: 'Yan Bînd!ga Da Dama Sun Miƙa Wuya Tare Da Ajiye Makamansu Bayan Gumurzu Da Sojoji, ida suka bukaci ayi Sulhu A Jihar Katsina.
Daga Comr Nura Siniya
Wasu shuwagabannin ‘yan bindigà waɗanda suka addabi yankin Batsari, Safana da Jibia a jihar Katsina, sun miƙa wuya tare da aje makamansu bayan gumurzu da sojoji, domin rungumar zaman lafiya.
Katsina Reporters ta samu cewa, shuwagabannin 'yan bin-digar da suka miƙa wuya, sun hada da ƙasurgumin dan fashin daji, Abu Radda, Umar Black da Abdullahi Lanƙai, Jijjige da kuma dabar Musa Ɗan gandu daga yankin garin Jibia a Katsina.
A cikin jawaban tubabbun 'yan bindigar sun nemi gwamnati ta duba bukatunsu wajen gina masu kasuwanni da asibitoci da kuma samar musu da ruwan sha, domin yin rayuwa mai inganci.
A yayin zaman kungiyar mutanen yankin da matsalar tsaro ta shafa, (NCSOSACK) karkashin jagorancin Comrd Hamisa S Batsari, sune suka wakilci al'ummar da matsalar tsaron ta shafa a yankunan.
A karshe, shuwagabannin ‘yan bin-digar sun miƙa makamansu ga sojojin, inda suka sako wasu mutanen da suka yi garkuwa da su tare da ɗaukar alkawarin rungumar zaman lafiya.














