MUTUWA WA'AZI NE
Mahaifin jarumar Hausa film Rahama Sadau ya rasu a yau, kuma har anyi jana'izarsa
Muna amfani da wannan dama wajen isar da sakon ta'aziyyah da nasiha ta 'yan uwantaka zuwa ga jaruma Rahama Sadau
Muna miki ta'aziyyah Allah Ya jikan Mahafinki, Allah Ya sa dan Aljannah ne, Allah Ya gafarta masa tare da dukkan 'yan uwa Musulmi da suka rigamu gidan gaskiya
A babi na nasiha zuwa gareki wannan mutuwa da aka miki ta isheki wa'azi, babu wani nasiha da za'a miki fiye da wannan
Rahama Sadau ki sani cewa hanyar da kike kanta ba hanya bace mai kyau da zata sa ki hadu da Allah lafiya, lokaci bai kure miki ba da zaki tuba ki gyara, ki watsar da harkan film da yawon duniya, kiyi aure ki rufa wa kanki asiri domin ki hadu da Allah Mahaliccinmu lafiya
Bani da wata hanya da zan isar miki da sakon ta'aziyyah da nasiha sai ta nan, idan nasihar tayi zafi kiyi hakuri
Allah Ya jikan dukkan Musulmi, Ya bamu ikon gamawa da duniya lafiya muna Musulmai masu imani























